in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wajibi ne a fahimci ayyukan da tilas ne a yi da kuma ci gaba da hada kai da gwagwarmaya, in ji shugaban kasar Sin
2012-11-09 17:18:50 cri

A jiya da safe ne aka bude babban taron wakilan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 18 a nan birnin Beijing.

Yau ranar 9 ga wata da safe, a yayin da yake tattaunawa da wakilan da suka fito daga lardin Jiangsu, Hu Jintao, shugaban kasar Sin ya nuna cewa, rahoton da jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta gabatar a yayin bikin bude taron ya kasance tamkar wata sanarwa da kuma matakan da aka tsara dangane da yadda za a samu sabuwar nasara a fannin raya gurguzu mai halin musamman na kasar Sin a cikin sabon halin da ake ciki. Don haka, wajibi ne a fara yin koyi da kuma aiwatar da tanade-tanaden da ke cikin wannan rahoto, kuma a fahimci nauyi da ayyukan da aka danka, a ci gaba da yin hadin gwiwa da gwagwarmaya, a kokarin kara samun nasara cikin babban sha'anin raya gurguzu mai halin musamman na kasar Sin. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China