Shugaban jam'iyyar PDP mai mulki a Najeriya, Alhaji Bamanga Tukur ya ce, kamar a kasar Sin, Jam'iyyar kwaminis ta Sin har kullum tana kokari sosai wajen kara kyautata zaman rayuwar jama'a, haka ma Jam'iyyar PDP tana gudanar da harkokin mulki a Nijeriya yadda ya kamata, sabo da haka tana son hada kai da Jam'iyyar Kwaminis ta Sin.
Shugaban na PDP ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke zantawa da wakilin sashen hausa na CRI a Abuja a gabannin babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18, inda ya ce PDP da JKS za su kara yin cudanya da juna
Ga cikakkiyar hirar da Dan Ladi, wakilin CRI a Abuja, tarayyar Nijeriya ya kawo mana.