in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18
2012-11-08 09:43:33 cri

Yau Alhamis 8 ga wata, a babban dakin taron jama'a, an bude babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin mai mulki karo na 18 a hukunce, kuma manyan shugabannin jam'iyyar da wakilan mambobin jam'iyya guda 2300 sun halarci taron.

A madadin kwamitin tsakiya karo na 17, babban sakatare kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Hu Jintao ya gabatar da rahoto, kuma wakilan jam'iyyar za su duba rahoton nasa. A cikin wannan rahoto, an ce, jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin za ta shugabanci kasar don tabbatar da ci gaba da bin hanyar gurguzu da ke da halayyen musamman na kasar Sin.

Babban taron wakilan jam'iyya da kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya zama hukumar koli ta jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma a kan yin taro a ko wadanne shekaru biyar-biyar. Yanzu, akwai mambobin 'yan jam'iyyar kwaminis da yawansu ya kai sama da miliyan 80, kuma wakilan mambobin 'yan jam'iyyar da yawansu ya kai sama da 2200 da aka zabe su sun halarci taron, kuma , wakilan mambobin 'yan jam'iyya da suka shiga jam'iyyar bayan da aka gudanar da manufar yin gyare-gyare da bude kofa ga kasashen waje a shekarar 1978 sun yi rinjaye a cikinsu.

Bisa ajandar taron, a cikin kwanaki 7 masu zuwa, wakilai mahalartar taron za su duba rahoton da Mr. Hu ya gabatar, kuma za a zartas da gyararren tsare-tsare na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, sannan za a duba rahoton da kwamitin ladabtarwa na jam'iyyar ya gabatar, gami da zaben sabon kwamitin tsakiya da sabon kwamitin ladabtarwa na kasar Sin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China