in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Jam'iyyar PDP ta Nijeriya yana son kara yin cudanya da Jam'iyyar Kwaminis ta Sin
2012-11-04 16:16:43 cri

Shugaban jam'iyyar PDP mai mulki a Najeriya, Alhaji Bamanga Tukur ya ce, kamar a kasar Sin, Jam'iyyar kwaminis ta Sin har kullum tana kokari sosai wajen kara kyautata zaman rayuwar jama'a, haka ma Jam'iyyar PDP tana gudanar da harkokin mulki a Nijeriya yadda ya kamata, sabo da haka tana son hada kai da Jam'iyyar Kwaminis ta Sin.

Shugaban na PDP ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke zantawa da wakilin sashen hausa na CRI a ran 1 ga wata a Abuja, inda ya ce PDP da JKS za su kara yin cudanya da juna

Alhaji Bamanga Tukur ya kara da cewa, a wannan wata za a gudanar da babban taro karo na 18 na Jam'iyyar Kwaminis ta Sin, kuma yana fatan za a kara yin mu'amala tsakanin jam'iyyun biyu domin taimakawa jama'ar bangarorin biyu.(Danladi, wakilin CRI daga Abuja, Nijeriya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China