in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tsayar ranar 8 ga watan Nuwamba don gudanar da babban taron JKS karo na 18
2012-09-28 20:27:48 cri
Hukumar kula da harkokin siyasa na kwamitin tsakiya na JKS ta yanke shawara a wani taron da ya gudanar a ranar Jumma'a don gabatar da shirin gudanar da taro karo na 7 na kwamitin tsakiya na JKS karo na 17 wanda za a gudanar a ranar 1 ga watan Nuwamba.

Taron hukumar karkashin jagorancin shugaba Hu Jintao, babban sakataren kwamitin tsakiya na JKS, ya yi nazarin abubuwan da ake saran gudanarwa a tarukan watan Nuwamba.

Babban taron wani muhimmin ganawa ce ta jam'iyyar da za a gudanar a wani muhimmin lokaci da kasar Sin ke kokarin gina al'umma ta gari daga dukkan fannoni, da gudanar da gyare-gyare a cikin gida tare da bude kofa ga kasashen waje, gudanar da canje-canjen tattalin arziki a fannoni daban-daban.

Babban taron zai kara bayyana tsarin gurguzu na musamman na kasar Sin, nazarin ayyukan da jam'iyyar ta gudanar cikin shekaru biyar da suka gabata da kuma abubuwan da jam'iyyar ta aiwatar tun babban taron jam'iyyar karo na 16.

Bugu da kari, taron zai yi nazarin darussan da jam'iyyar ta koya a baya daga lokacin da ta yi kokarin hada kan al'ummar kasar ta yadda ake jagorantar dukkan kungiyoyin kabilun kasar tare da ciyar da akidar kwaminisanci gaba.

Babban taron har ila, zai shata wasu manufofi da dakoki da za su dace da zamani tare da biyan bukatun al'umma.

A cewar taron, za kuma a zabi sabbin mambobin kwamitin tsakiya na JKS da sabuwar hukumar ladabtarwa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China