in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi kira da a yi kokarin kiyaye zaman lafiya a yankin Gulf
2012-01-19 16:55:55 cri
Ranar Alhamis 19 ga wata, a nan birnin Beijing, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Mista Liu Weimin ya ce, Sin tana kira ga bangarori daban-daban da su yi hakuri da nuna juriya, domin tabbatar da zaman lafiyar da kwanciyar hankali a yankin Gulf.

A 'yan kwanakin nan, wasu kasashen yamma suna kara kakabawa kasar Iran takunkumi, lamarin da ya tsananta halin da ake ciki a yankin Gulf. Mista Liu ya ce, kasar Sin tana ganin cewa hakan ba zai amfana wajen daidaita matsalar Iran ba, kuma tana nuna damuwa kan wannan batu.

Mista Liu ya kara da cewa, kasar Sin ta bada shawarar daidaita sabani da rikici tsakanin kasa da kasa ta hanyar yin shawarwari, kuma sanya takunkumi da kara matsa lamba har ma da yin barazana da karfin soji, sam ba za su taimaka wajen warware matsala ba, sai ma su tsananta halin da ake ciki.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China