Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasashen Afirka na kira a cire takunkumin da aka sanyawa Zimbabwe
2020-10-26 20:50:48        cri
Akwai kasashen Afirka da dama wadanda suka yi kira ga kasashen yammacin duniya su soke takunkumin da suka garkamawa Zimbabwe ba bisa doka ba. Game da wannan batu, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian ya bayyana cewa, kasarsa na goyon-bayan wannan kiran da kasashen Afirka suka yi.

Jiya Lahadi, rana ce da gamayyar raya kudancin Afirka wato SADC a takaice ta kebe a matsayin ranar nuna adawa da takunkumi, inda kasashen Afirka da dama suka yi kira a soke takunkumin da kasashen yamma suka sanyawa kasar Zimbabwe. Mista Zhao ya bayyana cewa, kamata ya yi Amurka da sauran kasashe da kungiyoyi, su cire takunkumin da suka sanyawa Zimbabwe, da daukar matakan da suka dace, domin taimakawa Zimbabwe yaki da annobar COVID-19, da ma farfado da tattalin arzikinta.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China