Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ministan Kudin Afirka ta Kudu: Raguwar tattalin arzikin bana zai wuce kaso 7 bisa dari
2020-09-14 13:40:46        cri
Ministan Kudi na Afirka ta Kudu Tito Mboweni, ya ce sakamakon yaduwar annobar COVID-19, raguwar tattalin arzikin kasarsa a wannan shekara, zai wuce kashi 7%, idan an kwatanta da hasashen da ma'aikatar kudin kasar ta yi a baya.

A 'yan kwanakin da suka gabata, alkaluman da gwamnatin Afirka ta Kudu ta fitar suka nuna cewa, yawan GDPn kasar, a rubu'i na biyu na shekarar bana ya ragu da kashi 51 %, raguwar da ba a taba ganin irinta ba a tarihin kasar. Wannan ne karo na 4 a jere da ake samun raguwar GDPn a cikin rubu'i hudu da suka gabata. Jami'in ya ce muhimmin dalilin da ya haifar da wannan raguwar, shi ne tsauraran matakan da aka dauka a kasar da nufin hana yaduwar COVID-19.

Mboweni wanda ya bayyana hakan a jiya Lahadi 13 ga wata, ya ce ana daukar tasirin hakan ga kamfanin samar da wutar lantarki na kasar Afirka ta Kudu, a matsayin wata babbar barazana ga tattalin arziki da harkokin kudin kasar.

Kwanan nan, kamfanin ya kara ba da umarnin takaita wutar lantarki a duk fadin kasar. Kaza lika jami'in ya bayyana cewa, gwamnatin kasarsa, za ta kaddamar da wani aiki na hadin gwiwa don hanzarta saurin farfadowar tattalin arziki, ta yadda za a cika alkawarin da gwamnatin kasar ta dauka ga al'ummar ta. (Bilkisu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China