Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Yawan wadanda suka kamu da COVID-19 a Afirka ya zarce miliyan daya
2020-08-07 19:48:23        cri

Cibiyar kandagarki da hana yaduwar cututtuka ta Afirka (Africa CDC) ta bayyana Jumma'ar nan cewa, yawan wadanda suka kamu da cutar numfashi ta COVID-19 a sassan nahiyar, ya zarce miliyan daya.

Africa CDC, kwararriyar hukumar lafiya ta hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Afirka mai mambobin kasashe 55, ta bayyana cikin rahoton ta na baya-bayan nan da take fitarwa game da yanayin cutar a sassan nahiyar cewa, yawan mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar a sassan nahiyar, ya karuwa zuwa 1,007,366 ya zuwa tsakar ranar yau.

Rahoton cibiyar ya nuna cewa, yawan mutanen da suka mutu sanadiyar cutar, ya karu daga mutane 21,617 a ranar Alhamis zuwa 22,066 a yau Jumma'a.

Kasar Afirka ta kudu ce cutar ta fi yiwa illa a nahiyar, inda ya zuwa yanzu aka tabbatar da mutane 538,184 da suka kamu da cutar, sai kasashen Masar da Najeriya da Aljeriya da Morocco dake biye mata baya.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China