Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ministan tsaron Sin ya zanta da takwaransa na Amurka ta wayar tarho
2020-08-07 10:08:34        cri
Mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kana ministan tsaron kasar, Wei Fenghe, a ranar Alhamis ya zanta ta wayar tarho tare da takwaransa sakataren harkokin tsaron Amurka Mark Esper, bisa ga bukatar da aka nema.

Bangarorin biyu sun yi musayar ra'ayoyi game da huldar dake tsakanin kasashen biyu, da dangantakar soji a tsakaninsu, kana da batun huldar musayar sojoji tsakanin kasashen biyu a zagaye na gaba.

Wei, ya bayyana matsayar kasar Sin game da wasu batutuwa da suka hada da batun tekun dake kudancin kasar Sin, da batun yankin Taiwan, da nuna kyamar da Amurka ke yiwa kasar Sin, inda ya bukaci bangaren Amurka da ta dena furta kalaman batanci ko kuma aikata mummunan aiki kan kasar Sin, a yi kokarin ingantawa da kuma tabbatar da harkokin tsaro dake shafar tekuna, kana a guji yin duk wani mummunan yunkuri wanda zai iya lalata yanayin da ake ciki, kuma a yi kokarin kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin shiyyoyin.

Esper a nasa bangaren yace, yayin da ake fuskantar zaman tankiya tsakanin kasashen biyu, ya kamata bangaren sojojin kasashen biyu su mayar da hankali kan tattaunawa da tuntubar juna domin warware duk wani sabani, kuma su guji yiwa juna mummunar fassara da kuma rage abubuwan da zasu haifar da barazana a tsakaninsu. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China