Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
MDD ta yi Allah wadai da kai hari kan jami'an bada agaji a yankuna masu fama da rikici a Kamaru
2020-06-05 10:48:32        cri
Hukumar kula da ayyukan jin kai ta MDD ta yi Allah wadai da babbar murya game da kai hari kan jami'an ba da agaji a yankuna masu magana da yaren Turanci dake fama da rikicin mayakan 'yan aware sama da shekaru uku a jamhuriyar Kamaru.

Allegra Baiocchi, shugabar kula da shirin bada agaji ta MDD a Kamaru ta ce, watanni biyun da suka gabata an samu karuwar hare haren inda aka bada rahoton hukumomin agaji shida anyi garkuwa da jami'ansu, ko kuma an tsaresu tare da yiwa rayuwarsu barazana.

Baiocchi ta fada cikin wata sanarwa da aka fitar a birnin Yaounde na kasar cewa, lamarin ya kai wani mataki inda masu aikin bada agajin sun shiga wani yanayi na rashin tabbas game da makomar rayuwarsu.

A cewar sanarwar, galibin garkuwar da mutane da ake samu, mayakan 'yan aware ne suke aikatawa, sannan dakarunn gwamnati suna fuskantar jinkiri wajen shigar da kayan agajin zuwa yankunan.

Jami'ar tayi gargadin cewa, hare haren da ake kaddamarwa kan ma'aikatan bada agajin ba za'a aminta ba tilas ne a kawo karshensa. (Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China