Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin za ta tura tawagogin ma'aikatan lafiya zuwa Zimbabwe da DRC da Aljeriya don yaki da COVID-19
2020-05-11 19:43:22        cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin ta yanke shawarar tura tawagogin ma'aikatan lafiya zuwa kasashen Zimbabwe, da Jamhuriyar demokiradiyar Congo, da Aljeriya, don taimakawa matakan kasashen na Afirka kan yaki da barkewar COVID-19.

A cewar Zhao, a safiyar yau Litinin 11 ga watan Mayu ne, tawagar lafiya daga kasar Sin ta tashi zuwa kasar Zimbabwe, daga bisani kuma, sauran tawagogin za su bar kasar Sin zuwa kasashen Jamhuriyar demokiradiyar Congo da Aljeriya. Ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da taimakawa kasashen na Afirka da kayayyakin yaki da wannan annoba bisa ga yanayin yaduwar cutar da ma bukatun kasashen na Afirka, yana mai jaddada hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin kiwon lafiyar jama'a da kandagarki da hana yaduwar cututtuka, da shiga a dama da ita a yakin da ake yi na ganin bayan wannan annoba baki daya.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China