Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ministan harkokin wajen Nijeriya ya musanta cewa ya kamu da cutar COVID-19
2020-03-31 10:21:16        cri

Ministan kula da harkokin wajen Nijeriya Geoffrey Onyeama ya musanta cewa ya kamu da cutar numfashi ta COVID-19.

Cikin wata sanarwar da ta shiga hannun kamfanin dillancin labarai na Xinhua jiya a Lagos, Ministan ya bayyana rahoton na wasu kafafen yada labarai dake zargin ya kamu da cutar a matsayin karya.

Ya ce a matsayinsa na mamban kwamitin ko-ta-kwana kan cutar, wanda shugaban kasar ya nada, an yi masa gwaji tare da sauran mambobin kwamitin a baya-bayan nan, kuma sakamakon ya nuna dukkansu ba su kamu da cutar ba.

Ya ce an san wadanda suka rubuta labarin na da manufar kunyata shi da kuma yada fargaba a lokacin da kasar ke fuskantar annobar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China