Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kididdigar COVID-19 ta ranar 19 ga watan Maris
2020-03-19 15:32:52        cri
Kasashen duniya suna cigaba da daukar matakan yaki da yaduwar cutar numfashi ta COVID-19, yayin da mutane sama da 200,000 suka kamu da annobar a fadin duniya, inda adadin mutanen da cutar ta hallaka ya zarce 8,000.

Babban daraktan hukumar lafiya ta duniya WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus ya sanar a ranar Laraba cewa, kashi 80 bisa 100 na yawan mutanen da suka kamu da cutar a duk fadin duniya daga shiyyoyi biyu ne, wato kasashen yammacin tekun Pacific da nahiyar Turai.

A bisa alkaluman hukumar ta WHO, adadin mutanen da suka kamu da cutar daga wajen kasar Sin ya kai 112,878 ya zuwa safiyar ranar Laraba.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China