Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Wang Yi ya yi bayani kan ziyarar aiki ta farko da shugaba Xi Jinping ya yi a sabuwar shekara
2020-01-19 17:00:28        cri
Tun daga ranar 17 zuwa 18 ga wannan wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyarar aiki a kasar Myanmar bisa gayyatar da aka yi masa. Yayin da aka gama ziyarar, memban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya yi bayani game da wannan ziyara. Wang Yi ya bayyana cewa, ziyarar aikin shi ne wani muhimmin aikin harkokin waje na kasar Sin, koda yake ba a shafe kwanaki da dama kan ziyarar ba, amma an samu nasarori da dama. Shugaba Xi Jinping ya halarci bukukuwa 12, da cimma yarjejeniyoyin hadin gwiwa 29 dake shafar fannoni daban daban, kana bangarorin biyu sun gabatar da hadaddiyar sanarwa.

Wang Yi ya bayyana cewa, bangarori daban daban na kasar Myanmar sun nuna yabo ga ziyarar aikin, sun yi tsammani cewa, a yayin da ake cika shekaru 70 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Myanmar da Sin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyarar aiki a kasar ta Myanmar, wadda ta kansance kasa ta farko da ya kai ziyara a sabuwar shekara, wannan ya shaida cewa, an sada zumunta a tsakanin kasashen biyu mai zurfi, da kuma bude sabon babi a wannan fanni. Kafofin watsa labaru na kasa da kasa sun kara maida hankali ga ziyarar aikin, sun yi tsammani cewa, aikin diplomasiyya da shugaban kasar Sin ya yi ya taimakawa sada zumunta a tsakanin Sin da Myanmar zuwa sabon matsayi, kana an samu babban ci gaba kan raya shawarar "ziri daya da hanya daya", ta hakan za a kara inganta tasirin Sin da aka kawo wa duniya baki daya.

Wang Yi ya kara da cewa, shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin ta tsaya tsayin daka kan manufar samun bunkasuwa cikin lumana, da kaucewa yin kama karya da tsoma baki kan harkokin cikin gida na sauran kasashe, Sin za ta ci gaba da yin magana domin nuna goyon baya ga kasashe masu tasowa a duniya. Sin ta nuna goyon baya ga kasar Myanmar da ta ci gaba da bin hanyar da ta zaba, da tabbatar da moriyarta da girmamawarta a dandalin duniya. Sin ta girmama ikon mallaka da burin kasar Myanmar, da taimakawa wajen sa kaimi ga samun zaman lafiya da sulhuntawar al'ummar kasar Myanmar. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China