![]() |
|
2020-01-14 20:24:48 cri |
Geng Shuang ya bayyana hakan ne a Talatar nan, yayin taron manema labarai da aka gudanar a nan birnin Beijing. Ya ce tsakanin ranekun 7 zuwa 13 ga watan Janairun nan, dan majalissar gudanarwa, kuma ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya ziyarci kasashen Masar, da Djibouti, da Eritrea, da Burundi da Zimbabwe.
Kaza lika a yayin wannan ziyara, Wang Yi da wasu shugabannin nahiyar, da takwarorin aikin sa na kasashen da ya ziyarta, sun yi musaya mai zurfi, tare da cimma matsaya guda a fannin yaukaka alakar su, da zurfafa hadin gwiwar cimma moriya tare. Ya ce dukkanin sassan biyu sun bayyana burin su na gaggauta aiwatar da sakamakon dandalin FOCAC da ya gabata na birnin Beijing, tare da ingiza hadin gwiwar aiwatar da manufofin dake kunshe cikin shawarar "ziri daya da hanya daya ", da kara hada karfi wajen aiwatar da hadin gwiwar su daga dukkanin fannoni. Dukkanin sassan dai na ganin Sin da Afirka, na cikin wani yanayi na kyawun dangantaka, yayin da makomar hadin gwiwar su ke kara haskawa. (Saminu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China