Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Shugabannin Turkiya da Amurka sun tattauna kan halin da kasashen Libiya da Sham ke ciki
2020-01-03 11:17:47        cri

Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya bugawa takwaransa na Amurka Donald Trump waya a jiya Alhamis don tattauna halin kasashen Libiya da Sham da dai sauransu ke ciki.

Fadar shugaban Turkiya ta ba da wata sanarwa a wannan rana cewa, tattaunawar da shugabannin biyu suka yi ta mai da hankali sosai kan muhimmancin matakan diplomasiyya wajen warware rikicin shiyya-shiyya, tare da amince da kara hadin kansu.

A nasa bangare, Trump ya ce, yadda wasu kasashen ketare ke tsoma baki a harkokin Libya na kara dagula halin da kasar ke ciki. Ban da wannan kuma, shugabannin biyu sun yarda da sassauta halin da ake ciki a jihar Idlib don kiyaye fararen hula. (Amina Xu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China