Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Morocco ta kama wani da take zargi da alaka da IS
2019-12-16 11:09:06        cri

Jami'an tsaron kasar Morocco sun cafke wani mutum da suke zargin yana da alaka da kungiyar masu da'awar kafa daukar Islama ta IS.

Mutumin mai shekaru 41, an kama shi ne a ranar Asabar a birnin Meknes. Ana zargin mutumin da yunkurin shirya harin kunar bakin wake, hukumar bincike game da shari'a, wato hukumar tattara bayanan sirri ta kasar Morocco ce ta bayyana a cikin wata sanarwa.

Sanarwar ta kara da cewa, an kwace dukkan wasu na'urori da wasu takardu dake da nasaba da shirin hada ababen fashewar daga wajen mutumin.

A binciken da aka gudanar, an gano cewa, mutumin da ake zargin yana da hannu wajen yada manufofin tsattsauran ra'ayi na kungiyar IS.

A cewar sanarwar, za'a gurfanar da wanda ake zargin gaban shari'a da zarar an kammala binciken da ofishin gudanar da binciken laifuka na kasar ke gudanarwa.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China