2019-12-14 15:55:29 cri |
A yayin ziyararsa, Ji Bingxuan ya bayana cewa, a cikin shekaru 55 da aka kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Sin da jamhuriyyar Congo, kasashen biyu sun nuna girmamawa, da daidaito, da kuma sahihanci ga juna, da kuma fahimtar juna da nuna goyon baya ga juna kan manyan batutuwan da suka mayar da hankali kansu. Sin tana son yin kokari tare da jamhuriyyar Congo wajen aiwatar da ayyukan da aka tsara a gun taron kolin Beijing na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka da shugabannin kasashen biyu suka cimma daidaito, ta hakan za a sa kaimi ga neman raya makoma ta bai daya tsakanin Sin da Afirka。
A nata bangare, kasar jamhuriyyar Congo ta nuna godiya ga kasar Sin domin ta samar da goyon baya gare ta wajen raya tattalin arziki da zamantakewar al'umma a kasar, kana za ta kara yin mu'amala da hadin gwiwa tare da kasar Sin a fannoni daban daban don amfanawa jama'arsu baki daya. (Zainab)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China