Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
AU ta koka kan matsanancin tasirin sauyin yanayi dake addabar Afirka
2019-12-12 11:06:31        cri
Wata sanarwa da kungiyar tarayyar Afirka ta AU ta fitar a jiya Laraba, ta tabbatar da karuwar tasirin sauyin yanayi a kasashen dake nahiyar cikin shekaru kusan 20 da suka gabata. Sanarwa ta ce hakan na yin mummunan tasiri ga zamantakewa da tattalin arzikin kasashen nahiyar.

AU ta ce duk da irin ci gaba da ake samu a fannin raya tattalin arziki da jin dadin jama'a a nahiyar, har yanzu Afirka na da rauni game da tunkarar matsalolin sauyin yanayi, tana kuma gamuwa da bala'u daban daban masu nasaba da sauyin yanayi. Kaza lika wannan matsala na yin tarnaki ga burin cimma ajandar kasashenta nan da shekarar 2063, da ma kudurorin dake kunshe cikin shirin samar da ci gaba mai dorewa na kasa da kasa ko SDGs a takaice.

A baya bayan nan ma dai, bankin duniya ya fitar da wani rahoto, wanda ya bayyana irin yadda kasashen Afirka da dama suka cimma manyan nasarori cikin gwamman shekarun da suka shude, inda matsakaicin alkaluman ci gabansu ya karu da kaso 4.5 bisa dari, to sai dai kuma sauyin yanayi mai nasaba da karuwar zafi ko raguwarsa, da yanayin ruwa, da sauran bala'u masu aukuwa sakamakon hakan, na barazana ga wannan ci gaba.

Sanarwar ta AU ta ce, kungiyar na jaddada muhimmancin aiwatar da yarjejeniyoyin kasa da kasa na dakile tasirin sauyin yanayi, wadanda suka hada da yarjejeniyar Paris, da tsarin aiki na Sendai, da kudurorin wanzar da ci gaba na SDGs, da ajandar "New Urban". (Saminu Hassan)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China