2019-11-13 11:04:49 cri |
Haka zalika, David Monyae, ya ce kasar Sin, bisa matsayinta na tattalin arziki mafi karfi tsakanin kasashen BRICS, tana taka muhimmiyar rawa, a kokarin tabbatar da tsarin hadin gwiwa na BRICS. Ya ce kasar Sin tana samar da goyon baya a fannonin kudi, da ilimi, gami da tsare-tsaren raya kimiyya da fasaha.
A ganinsa, jarin da kasar Sin ke zubawa nahiyar Afirka, zai taimaka wa kasashen dake nahiyar raya kansu, gami da cimma burinsu na samun ci gaba mai dorewa, wanda ya shafi dukkan bangarorin al'umma. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China