Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Tsohon jami'in Najeriya: harkokin Hong Kong harkokin cikin gida ne na Sin, sauran kasashe ba su da ikon tsoma baki a ciki
2019-10-17 13:53:45        cri
Tsohon karamin jakadan Najeriya dake yankin Hong Kong na kasar Sin Ahmed Gusau Bala ya bayyana a kwanakin baya cewa, tashe-tashen hankula da suke faruwa a Hong Kong a kwanakin nan abun mamaki ne da bakin ciki, batun Hong Kong harkokin cikin gida ne na kasar Sin, sauran kasashe ba su da ikon tsoma baki a ciki.

Ahmed Gusau Bala ya taba zama karamin jakadan Najeriya dake Hong Kong a tsakanin shekarun 2017 - 2018. A yayin da yake zantawa da wakilinmu ya ce, ana gudanar da tsarin "kasa daya, tsarin mulki guda biyu" yadda ya kamata a yankin Hong Kong. Game da zanga-zangar nuna karfin tuwo da ayyukan lalata kayayyaki da aka ta yi na tsawon 'yan watanni a yankin, Bala ya ce, nuna karfin tuwo ba zai taimaka wajen warware duk wata matsala ba, rahotannin da wasu kafofin watsa labaru suka bayar da kalaman 'yan siyasa na yammacin duniya son zuciya ne. Harkokin yankin Hong Kong harkoki ne na cikin gidan kasar Sin, sauran kasashe ba su da ikon tsoma baki ciki. (Bilkisu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China