Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ci gaban da Sin ta samu cikin shekaru 70 da suka gabata abin koyi ne
2019-09-05 10:30:10        cri

Wata kungiyar kwararru ta kasar Zambiya ta ce, ci gaban da kasar Sin ta samu a cikin shekaru 70 da suka gabata ya samar da muhimmin darasi ga kasashen Afrika wadanda ya kamata su dau izina.

Chenai Mukumba, mai sulhuntawa dake aiki a cibiyar kasa da kasa ta kungiyar masu sayayya (CUTS), ta ce babu shakka, ci gaban da kasar Sin ta samu a cikin shekaru 70 ya haifar da muhimmin sakamako, matakin da ya baiwa kasar damar zama kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya.

Ta ce hakika, shugabannin kasar Sin sun yi kyakkyawan tanadi na ganin kasar ta samu nasarori a cikin shekaru 70 din da suka gabata, ya kamata mu koyi darasi game da yadda wannan shiri ya kai ga nasara.

Ta kara da cewa, a halin yanzu kasar Sin ta fita zuwa kasashen ketare inda ta zuba jari a sauran kasashen duniya, kuma ta zuba jari mai dunbun yawa a fannin ayyukan gina kayayyakin more rayuwa, musamma a kasashen Afrika.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China