Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Harin Boko Haram ya hallaka manoma 6 a jihar Bornon Najeriya
2019-07-18 19:44:58        cri

A kalla manoma 6 ne aka tabbatar sun rasu, sakamakon wani hari da wasu mahara da ake tsammanin mayakan Boko Haram ne suka kaddamar, a yankin Muna Dalti, mai nisan kilomita 6 daga birnin Maiduguri, fadar mulkin jihar Borno ta arewa maso gabashin Najeriya.

Rahotanni daga rundunar sojojin kasar sun nuna cewa, an hallaka manoman ne a ranar Laraba, lokacin da 'yan bindigar suka aukawa yankin, suna tsaka da aiki a gonakin su. Majiyar rundunar sojojin ta ce mayakan na Boko Haram, sun kutsa kai cikin yankin ne a kan babura.

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, shugaban dakarun dake tallafawa ayyukan yaki da kungiyar ta Boko Haram ko Civilian JTF a takaice Sheriff Danfulani, ya nuna matukar damuwa, game da yadda 'yan ta'addan suka samu damar kaiwa wannan yanki hari har karo biyu a baya.

Danfulani ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, a lokutan baya, mayakan na Boko Haram, sun yi awon gaba da abinci da dabbobin da suka kwashewa manoman.(Jamila)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China