![]() |
|
2019-06-17 12:09:05 cri |
Direktan sashen nazarin harkokin Sin na cibiyar nazarin siyasa da kafofin watsa labaru ta kasar Masar Imad Azrak ya bayyana cewa, shugaba Xi Jinping ya hada da batun kiyaye tsaro da samun ci gaba tare, kana ra'ayinsa zai taimakawa wajen raya nahiyar Asiya mai yin imani da juna a fannin siyasa, ta hakan za a daidaita matsalolin rashin daidaito kan tattalin arziki a tsakanin yankunan nahiyar, har ma za a sa kaimi ga samun ci gaba a duk duniya baki daya.
Mai nazari na sashen nazari kan yankin gabas na cibiyar kimiyya da fasaha ta Rasha Vasily Kashin ya bayyana cewa, a cikin jawabin shugaba Xi, ya bayyana fatan Sin na more damar samun ci gaba tare da kasa da kasa, da kara samar da sharadi ga bangarori daban daban wajen shiga kasuwar kasar Sin, wadannan manufofi suna matukar jawo hankalin kasa da kasa. (Zainab)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China