Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin da Tajikistan sun amince su zurfafa mu'amala don samun kyakkyawar makomarsu
2019-06-16 17:03:03        cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Tajikistan Emomali Rahmon a ranar Asabar sun gudanar da tattaunawa, inda suka amince su kara zurfafa huldar kasashen biyu domin cimma nasarar samun bunkasuwa da kyakkyawar makoma tsakanin kasashen biyu.

Har wa yau, a wannan rana, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kuma karbi lambar yabo ta girmamawa, wadda itace lambar yabo mafi daraja a kasar Tajikistan, kuma shugaban kasar Tajik Emomali Rahmon ya mika lambar yabon ga shugaba Xi.

A lokacin bikin wanda aka gudanar a fadar shugaban kasar, Rahmon yayi cikakken bayani game da irin muhimmiyar gudunmowar da shugaba Xi ke bayarwa wajen raya cigaban dangantakar dake tsakanin Sin da Tajikistan, yace a shiye yake ya yi aiki tare da Xi wajen gina kyakkyawar alakar dake tsakanin kasashen biyu domin cimma manyan nasarori.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China