in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ra'ayina dangane da cikon shekaru 46 da kafa dangantakar jakadanci tsakanin Sin da Najeriya
2017-02-09 16:51:03 cri
Shekaru 46 da kafuwar huldar jakadanci da kuma diplomasiyya da abokanta, ta zama tamkar abokantaka mai yalwa da fahimtar juna da kuma hadin kai tsakanin taraiyar Nigeria da jamhuriyar jama'ar Sin. Cikin shekaru 46, kasashen Nigeria da China sun cimma matakan moriya mai yawa kana al'ummomin kasashen 2 sun shaida wannan moriya da yadda ya kamata. Kasar Sin ta yi mu'amula mai kyau kuma mai tagomashi mai yalwa tare kara fadada huldar abokantaka ta masamman. Kasar Sin ta bada muhimmiyar gudumowa sosai wajen ingiza bunkasuwar tattalin arzikin taraiyar Nigeria, al'amarin da ya bada muhimmin sakamako mai inganci da nagarta yayinda kamfanunuwan kasar Sin ke ci gaba da gudanar da aiyukan raya kasa a duk fadin taraiyar Nigeria.

A jihar Yobe alal misali, wani kamfanin kasar Sin mai suna CCECC na gudanar kyakkyawan aikin shinfida kwantar da gwamnatin taraiyar Nigeria ta ba su kwangilar yi a garin Gashua zuwa karamar hukumar Nguru aikin dake wakana a cikin yanayin aiki mai nagarta da inganci. Har wa yau, shekaru 3 da suka wuce, wani kamfanin kasar Sin mai aikin shinfida kwaltar mota ya yi aikin shinfida kwalta mai kyau daga garin Gashua zuwa karamar hukumar Yusufari, lamarin daya samu babban yabo ga kamfanin da ma kasar Sin kana al'ummar karamar hukumar Yusufari dake jihar Yobe sun samu saukin yin tafiye-tafiye. A shekarar 2016, a lokacin da kasashen Nigeria da China suka gudanar da bukukuwan murnar cikon shekaru 45 da kafuwar huldar jakadanci da diplomasiyya, shugaban taraiyar Nigeria ya kai ziyarar sada zumunci a birnin Beijing na kasar Sin inda shugaba Buhari ya yi shawarwari da mahukuntan kasar Sin kana shugabannin kasashen 2 suka taya juna murna kana suka cimma wasu yarjejeniyoyi da juna da suka shafi harkokin tsaro da kuma tattalin arziki.

Dan haka, ina taya kasashen 2 murnar cikon shekaru 46 da kafuwar huldar diplomasiyya da abokantaka da juna a cikin yanayin martaba tagomashin juna tare da yin aiki tare dan amfanuwar kasashen 2 da al'ummominsu.

Daga Alhaji Ali kiraji Gashua, jihar Yobe, tarayyar Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China