Za a kaddamar da taron shekara shekara na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa da na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ba da jimawa ba, inda firaministan kasar Sin Li Keqiang, zai gabatar da rahoton aiki ga majalisar wakilan jama'ar kasar Sin a madadin sabuwar gwamnatin kasar, tare da kira taron manema labaru, domin amsa tambayoyin 'yan jarida na gida da na waje, dangane da harkokin cikin gida da na wajen kasar ta Sin.
A sakamakon haka, yanzu sashen Hausa na CRI na gudanar da wani shiri na musamman mai taken "Ina da tambaya ga firaministan kasar Sin" a shafinmu na yanar gizo, da fatan za ku aiko mana da tambayoyinku kan adreshin na mu na E-mail, wato Hausa@cri.com.cn. Sai mun ji daga gare ku.