Ba shakka wannan abin yabawa ne tare da jinjinawa ga gwamnatin kasar Sin da dukkanin al'ummarta wajen kare martabar kayayyakin tarihi da alabun kasa baki baya wannan ya nuna azahiri dacewa kasar Sin kasa ce mai dadadden tarihi.
Abu na biyu shi ne mun zagaya a filayen wasannin olympic da kasar Sin ta gina a lokacin gasar, wadannan wurare muna jin labarinsu ne tun lokacin da kasar Sin ta sami damar daukar wannan gasa har aka kammala su aka soma wasannin olympic duk muna biye da gidan rediyon CRI yana fayyace muna yadda abubuwan ke gudana haka ma muna karanta mujallun kasar Sin, musanman na gidan rediyon CRI, muna samun labaru amma ba mu taba ganinsu ba sai a yau da muka zagaya tare da masaukinmu muka ga abubuwa masu ban sha'awa, a gaskiya wannan abu ya burge ni.
Daga karshe ina mika godiyata ta musamman ga shugaban sashen Hausa malam sanusi da kuma masu yi muna jagora malam Fatima da malama Zainab a kan jan namijin kokarinsu da suka nuna muna suka zagaya da mu a ko ina suka nuna muna wurare daban daban ina mai godiya a gare su tare da fatar Allah ya kara dankon zumunci tsakanimmu da wannan gidan rediyo amin na gode nagode. (SHUGABA BELLO ABUBAKAR MALAM GERO)