in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Abdulla Abbas, musulmi dan kabilar Tatar ya yi kira da a ba da kariya ga bishiyoyi domin hana kwararowar hamadar Tarim
2010-03-13 21:34:16 cri

Kabilar Tatar wata karamar kabila ce ta kasar Sin da ke bin addinin Musulunci, 'yan kabilar Tatar suna zama a jihar Xinjiang da ke arewa maso yammacin kasar. A matsayinsa na wakilin 'yan kabilar daya tak, Abdulla Abbas, furfesa na jami'ar Xinjiang ya dora muhimmanci sosai kan kiyaye muhallin halittu na jihar Xinjiang.

Malam Adulla ya furta cewa, yayin da yake yin bincike a kudancin jihar Xinjiang, ya gano cewa, ruwa ya kare a wani yanki na kogin Tarim, bishiyoyi masu dimbin yawa da ke kewayen hamadar Tarim sun mutu, adun da ya haddasa kwararowar hamada, da kuma tsanantar yanayin biranen da ke kusa da hamadar. Ban da wannan kuma, sakamakon karancin kirare, manoma da ke zama a kewayen hamadar sun sare bishiyoyi da yawa, wanda ya tsananta halin da hamadar Tarim ke ciki. Don haka Abdulla Abbas ya ba da shawarar kiyaye muhallin halittu na wurin domin hana kwararowar hamada. Ya ce,"Ya kamata a yi amfani da ruwan da ke cikin matarin ruwa wajen yin ban ruwa ga bishiyoyi, da kuma hana a raya gonaki marasa amfani ba bisa doka ba. A waje daya kuma ya kamata a aika da iskar gas zuwa ko wane gidan manoma da ke kewayen hamadar Tarim, ta yadda za a iya kyautata zamansu da kuma kiyaye muhallin halittu."(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China