in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jihar Ningxia tana kokarin kafa unguwar tattalin arziki da ke budewa zuwa ga yankunan Musulunci na duniya
2010-03-08 20:35:12 cri

A ran 5 ga wata, Mr. Wang Zhengwei, wakilin jama'ar kasar Sin, kuma shugaban gwamnatin jihar Ningxia ta kabilar Hui ta kasar ya bayyana a nan birnin Beijing, cewar jihar Ningxia tana kokarin kafa unguwar tattalin arziki da ke budewa zuwa ga yankunan Musulunci na duniya domin kokarin samun sabon ci gaba wajen bude kofa ga kasashen duniya.

Mr. Wang ya ce, za a yi kokarin raya dandalin tattaunawar hadin gwiwar cinikayya a tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa da gina wani zaunannen dakin dandalin. Haka kuma, jihar Ningxia tana yin hadin gwiwa da Dubbai wajen kafa kwalejin Confucius. Sannan jihar tana kokarin kafa wata unguwa, inda ba za a rika buga haraji ba ga kayayyakin Musulmai domin raya masana'antun musulmai a jihar.

Mr. Wang ya kara da cewa, an riga an kafa unguwannin masana'antu biyu a jihar Ningxia, wato unguwar raya kayayyakin abinci na Musulunci da unguwar samar da kayayyaki ga musulmai domin jawo masu tafiyar da masana'antun samar da kayayyaki ga musulmai da su zo jihar Ningxia. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China