Kasar Sin Ta Mayarwa Amurka Martani Kan Manyan Laifuka Biyar Na Keta Hakkin Dan Adam Da Take Aikatawa
2021-04-07 19:48:04 CRI
Kasar Sin ta mayarwa Amurka martani, bayan da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Amurka ta tsaya kai da fata cewa, takunkumin da ta kakaba wa kasar Sin, ya dace wajen hana gwamnatin kasar Sin keta hakkin dan Adam da aikata kisan kiyashi a yankin Xinjiang.
Sai dai mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasa Sin, Zhao Lijian, ya karyata zargin, yana mai cewa, batun aikata kisan kiyashi, karya ce tsagwaranta.
Daga nan, sai ya zayyana “manyan laifuffuka biyar” da gwamnatin Amurka ta aikata a cikin karnin da suka gabata, kama daga kisan ‘yan asalin Indian a karni na 19 zuwa nuna wariyar launin fata da raba kan al’umma.(Ibrahim)
Labarai Masu Nasaba
- Kasar Sin Ta Kare Sanarwar Da Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Turkiya Ya Wallafa A Shafin Tiwita Game Da Xinjiang
- Ziyara zuwa jihar Xinjiang
- Al'ummomi daban-daban na jin dadin rayuwa a jihar Xinjiang
- Sin: Har Yanzu Xinjiang Na Fuskantar Barazanar Ta’addanci Da Tsattsauran Ra’ayi Duk Da Rashin Kai Wani Hari Cikin Shekaru 4