MDD: Sama da mutum 63,000 suka tserewa gidajen su a Tigray
2020-12-16 11:54:11 CRI
Kakakin babban magatakardar MDD Stephane Dujarric ya ce sama da mutum 63,000 ne tashe tashen dake aukuwa a yankin Tigray na kisar Habasha ya raba da muhallansu, kuma MDD na fatan tantance hakikanin yawan su, da zarar jami’an ta sun samu ikon shiga yankin.
Stephane Dujarric, ya bayyana hakan ne a jiya Talata, yayin zantawa da manema labarai, yana mai cewa MDD na ci gaba da tuntubar bangaren gwamnatin Habasha, don tabbatar da shigar da kayayyakin jin kai ga yankin. A hannu guda kuma, jami’an MDD dake aiki a Sudan mai makwaftaka da Habashan, sun ce har yanzu suna fuskantar kalubale, game da taimakawa ‘yan gudun hijirar Tigray dake yunkurin tsallaka iyakar Habasha.
Bugu da kari, ana fuskantar karancin ruwan sha da kayan tsaftar muhalli, a cibiyoyin yada zango, da sansanin Um Raquba, mai karbar ‘yan gudun hijira sama da 16,000 da aka sake tsugunarwa.
Sama da mutane 50,000 ne suka tsere zuwa Sudan, tun bayan barkewar tashin hankali a Tigray a farkon watan Nuwamba, lokacin da ‘yan tawayen yankin suka fara dauki ba dadi da dakarun gwamnatin tarayyar Habasha, lamarin da ya katse shigar muhimman kayayyakin bukatar fararen hula, kuma hakan ya tilasawa dubun dubatar al’ummun yakin yin hijira, a gabar da kuma ake fama da karancin ababen bukata na yau da kullum, a sansanonin karbar ‘yan gudun hijirar. (Saminu)
Labarai Masu Nasaba
- Sudan ta jaddada goyon bayanta ga shugabanci AU dangane da batun madatsar ruwan Nilu na Habasha
- An fara aikin ginin hedkwatar hukumar dakile cutuka ta Afrika CDC a Habasha bisa tallafin kasar Sin
- Jami’an diflomasiyya na Habasha da Zimbabwe dake nan kasar Sin: Jari daga kasar Sin yana da muhimmanci sosai ga kasashensu
- Antonio Guterres ya nuna damuwa kan halin da ake ciki a yankin Tigray na Habasha