in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya halarci taron kasa da kasa na hadin gwiwar kasashe uku
2019-05-10 20:36:03 cri
Dan majalisar zartarwar kasar Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya ce kasar sa na da burin sauraro, da koyi daga shawarwari daga takwarorin ta Japan da Koriya ta kudu, ta yadda sassan uku za su ci gaba da hadin gwiwa karkashin shawarar ziri daya da hanya daya.

Wang Yi ya bayyana hakan ne, yayin da ya halarci taron bude dandalin kasa da kasa na shekarar 2019 na hadin gwiwar kasashen uku a Juma'ar nan.

Ya ce bana ake cika shekaru 20 da kulla huldar kawancen sassan uku, wato Sin da Japan da Koriya ta Kudu, don haka a cewar sa, kawancen sassan uku ya kai wani sabon matsayi a tarihi. Ya kara da cewa, Sin a shirye take ta yi aiki tare da Japan, da Koriya ta Kudu wajen bunkasa hade shiyyar su da ci gaban ta baki daya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China