in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana goyon bayan MDD ta hanyar wani takamaiman mataki
2019-05-09 09:28:51 cri
Wani rahoton da zaunanniyar tawagar kasar Sin a MDD ta gabatar ya sheda cewa, ya zuwa ranar Talata da ta gabata, wasu kasashe 40, ciki har da kasar Sin, sun biyan karo-karon kudin da MDD ke bukata domin gudanar da ayyukanta.

A cewar tawagar kasar Sin, ko da yake kason kudin da kasar Sin ke bayarwa ya karu sosai, amma kasar ta biya dukkan kudaden da ake bukata a shekarar 2019 cikin lokaci, ba tare da gindaya wani sharadi ba. Hakan ya nuna cewa, kasar Sin babbar kasar ce mai tasowa dake daukar nauyin da aka dora mata, wadda kuma ke goyon bayan MDD a harkokinta daban daban, musamman ma kan tsarin kasancewar bangarori daban daban a duniya. Wannan matakin da kasar Sin ta dauka ya sa ta samu yabo daga daukacin mambobin MDD, gami da sakatariyar majalisar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China