Kakakin rundunar reshen jihar Zamfara Muhammed Shehu ya tabbatar da aukuwar harin, yana mai cewa yanzu haka an tsaurara tsaro a yankin, tun bayan aukuwar wannan hari na ranar Asabar. Ko da yake bai yi karin haske game da hakan ba, amma ya ce akwai karin wasu mutanen da suka jikkata yayin harin.
Wasu al'ummar yankin sun bayyana cewa, harin na ranar Asabar ya auku ne yayin da al'ummar kauyen ke halartar wani bikin suna.
Dagacin kauyen na Dungurgu Hussaini Umar, ya ce maharan sun bullo ne ta wani daji a kan Babura, inda nan take suka bude wuta, suka tarwatsa taron mutanen dake bikin suna.