Kasar Sin za ta gudanar da taron don cika shekaru 100 da zanga-zangar ranar 4 ga watan Mayu
Kasar Sin na shirin gudanar da taron tunawa da cika shekaru 100 da gudanar da zanga-zangar da aka yi a ranar 4 ga watan Mayun shekarar 1919 a nan Beijing, da misalin karfe 10 na safiyar ranar Talata mai zuwa a babban dakin taron al'umma na Beijing.
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping, kuma babban sakataren kwamitin tsakiya na JKS, kana Shugaban rundunar sojin kasar, zai halarci bikin tare da gabatar da muhimmin jawabi. (Fa'iza Msutapha)