in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Djibouti: Shawarar ziri daya da hanya daya ya dace da moriyar kasashen biyu
2019-04-26 10:57:53 cri
A jiya ne, shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh, wanda a halin yanzu ke halartar taron kolin dandalin hadin gwiwar kasa da kasa karo na biyu a nan birnin Beijing, ya halarci taron murnar cika shekaru 40 da kulla huldar diplomasiyya a tsakanin kasarsa da kasar Sin, kuma taron murnar cika shekaru 42 da samun 'yancin kan kasar ta Djibouti. Ya jaddada cewa, shawarar ziri daya da hanya daya ta dace da moriyar kasashen biyu.

A jawabin da ya gabatar, shugaban ya ce, tun lokacin da kasashen biyu suka fara hadin gwiwa da juna a fannin harkokin diplomasiyya, kawo yanzu hadin gwiwarsu ta kai wani babban matsayi. Ya ce, kasashen biyu sun aiwatar da hadin gwiwar samun moriyar juna bisa la'akari da moriyar kasashen biyu. Sabo da haka, shawarar ziri daya da hanya daya da kasar Sin ta gabatar ta dace da moriyar kasar Sin, da ta kasar ta Djibouti.

Shugaban ya kara da cewa, kasar Djibouti na da damar samun babban kason cinikin teku da ake gudanarwa bisa la'akari da yankin da take, kuma za ta yi amfani da wannan dama, ta samar da yanayin ciniki mai inganci. Ya kara da cewa, kasarsa na matukar bukatar jari a fannonin harkokin yawon shakatawa da makamashi da kuma manyan ayyuka, kuma tana fatan amfana da wannan dama.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China