in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin jiragen saman Habasha na duba yiwuwar sayen jirage kirar kasar Sin na C919
2019-04-18 20:28:42 cri
Shugaban kamfanin zirga-zirgar jiragen saman fasinja na kasar Habasha (ET) Tewolde Gebremariam, ya sanar a yau Alhamis cewa, kamfanin na duba yiwuwar sayen jiragen fasinja kirar kasar Sin na C919.

Gebremariam wanda ya bayyana hakan yayin zantawarsa da kamfabnin dillancin labarai na Xinhua, ya ce kamfanin ET ya kuma kafa wani kwamitin hadin gwiwa da takwaransa na kasar Sin don duba irin ci gaban da aka samu game da sayen jiragen na C919.

Jami'in ya kuma bayyana cewa, kamfanin jiragen saman na ET yana aiki da gwamnatin kasar Sin , don mayar da Addis ababa, babban birnin kasar ta Habasha, a matsayin cibiyar fasahar kere-keren jiragen sama na kasar Sin a Afirka da kuma tsakanin Sin da Afirka a wannan fannin.

Ya kara da cewa, birnin Addis Ababa ba kawai zai zama wurin yada zangon jirage da kayayyaki ba, amma har ma zai zama cibiyar raya fasahar kere-keren jiragen saman kasar Sin a Afirka.

Kamfanin COMAC dai shi ne, babban kamfanin kera jiragen saman fasinja na kasar Sin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China