in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya aikawa takwaransa na Faransa sakon ta'aziyya dangane da gobarar Notre Dame
2019-04-16 20:16:27 cri
A yau Talata ne, shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya aikawa takwaransa na kasar Faransa Emmanuel Macron sakon ta'aziyya, bayan da mummunar gobarar nan da ta tashi a majami'ar Notre-Dame da ta shahara a duniya dake birnin Paris.

Shugaba Xi ya ce, Notre-Dame wata muhimmiyar alama ce ta wayewar kan kasar Faransa kana babbar albarkar wayin kan bil-Adama.

Kamar Faransawa, al'ummar Sinawa ma sun kadu matuka da bala'in gobarar. Ya ce, kasar Sin ta yi imanin cewa, za a gudanar da aikin gyara majami'ar yadda ya kamata, kuma za a sake dawo da kimarta bisa kokarin al'ummar Faransa tare da goyon bayan al'ummomin kasashen duniya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China