Da yake karin haske cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, mai magana da yawun rundunar sojojin Najeriya Sagir Musa, ya ce, sojojin sun yi dauki ba dadi da mayakan ne a yankin arewacin kauyukan Wulgo, Tumbuma, da Chikun Gudu da Bukar Maryam, dukkansu a bangaren Najeriya.
Sai dai Musa ya ce, babu wani sojin da ya rasa ransa daga bangaren kasashen biyu. A cewarsa, ana ci gaba da kai hare-haren hadin gwiwa, musamman a yankin Gombaru-Ngala da yankunan dake kawaye da shi, domin yakar mayakan da suka arcewa barin wutar da dakarun hadakar kasashen Najeriya da Benin da Chadi da kuma Jamhuriyar Nijar ke yi kan mayakan.(Ibrahim)