Dakarun gwamnati da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya zanta da su, sun tabbatar da faruwar arangamar, tare da jaddada cewa, wata tawaga tana can na ci gaba da kokarin dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin.
Sai dai sakataren watsa labaran 'yan awaren Cris Anu, ya aike da sakon murya ranar Lahadin da ta gabata a shafinsa na WhatAspp, yana mai gargadin cewa, yankin na cikin hadari. Don haka, ya bukaci mazauna Bali, da su fice daga yankin don tsira da rayukansu.(Ibrahim)