Ministan ya zargi wasu bangarori na kasashen waje da kungiyoyin dake da alaka da kungiyar kwararru ta Sudan da bangaren adawa da karban kudade masu yawa domin gudanar da zanga-zanga a kasar.
Ya kuma zargi bangaren adawar da kin amincewa da tattauanawa da gwamnati.
Ya ce rashin amincewa da tattaunawa da gwamnati ba tare da bayar da kwararan dalilai ba ya nuna cewa bangaren adawar na bukatar hambarar da gwamnati ne kawai. (Fa'iza Mustapha)