in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu a hare hare ta sama da Saudiyya ta jagoranta a Yemen ya kai 11
2019-04-08 10:06:18 cri
Ma'aikatar lafiyar a yankin da 'yan tawayen kasar Yemen ke rike da ikonsa ta sanar da cewa, adadin mutanen da suka mutu a wasu hare hare ta sama wanda dakarun kawancen da Saudiyya ke jagoranta suka kaddamar a Sanaa, babban birnin Yemen ya karu zuwa mutane 11, sannan wasu mutanen 30 sun samu raunuka.

A cewar mazauna yankin, an kaddamar da haren haren ta sama ne da rana tsaka, inda aka yi kokarin afkawa wata masana'antar hada karafu dake kusa da wata makaranta a yankin Sawan da ke gabashin birnin Sanaa.

Yousif al-Hadri, kakakin ma'aikatar lafiya a yankin dake hannun 'yan tawayen yace, adadin mutanen da suka mutu ya karu daga mutum 5 zuwa 11, "yawancinsu mata ne 'yan makaranta," wadanda aka raunata kuma ya karu zuwa 39, wanda har ya shafi wasu mutanen dake wucewa ta yankin.

Kakakin ya bayyana cewa, an shirya kai harin ne kan makaranta. An hana 'yan jaridu damar shiga inda lamarin ya faru tun bayan kaddamar da hare haren ta sama.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China