Labarin da jaridar Leadership A Yau ta samar a shafinta na internet ya nuna cewa, Sarakunan Gargajiya na al'ummar Hausawa mazauna jihar Ogun a karkashin jagorancin mai martaba Sarkin Hausawan jihar Ogun Alhaji Hasan– Hasan Abeokuta ta nada Alhaji Zakiru Mohmmed Bulanyaki karamar Hukumar Shagari ta jihar Sakkwato a matsayin Sarkin al'ummar Hausawa mazauna unguwar Asese ta karamar hukumar Obafemi Auwode a jihar Ogun, tare da magadansa guda uku. Magaddan sun hada da Alhaji Abubakar Lolo a matsayin garkuwan sarki Hausawa Asese a jihar Ogun da Alhaji Bala Mohammed a matsayin magajin garin Asese da Alhaji Umar Aliyu a matsayin Sarkin Yakin Asese kuma taron nadin sarautar ya gudana ne a cikin makarantar primary ta garin Asese sannan kuma taron ya samu halartar Sarakunan al'ummar Hausawa na jihar Ogun da na Legas da ma'aikata 'yan kasuwa.