in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya tattauna da takwararsa ta New Zealand kan yadda za su bunkasa alaka
2019-04-01 20:41:55 cri
A yau ne firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya tattauna tare da takwararsa ta kasar New Zealand, Jacinda Ardern wadda ke ziyara a kasar Sin, inda sassan biyu suka amince su karfafa alaka da ma tsarin cinikayya tsakanin kasashen duniya bisa doka.

Bugu da kari, sassan biyu sun yi musayar ra'ayoyi kan batutuwan kasa da kasa da na shiyya-shiyya dake shafarsu. Sun kuma kalli yadda aka sanya hannu kan muhimman takardun hadin gwiwa kan haraji da aikin gona da harkokin kudi da binciken kimiyya. Daga bisani kuma su ka fitar da sanarwa kan matsalar sauyin yanayi.

A jiya Lahadi ne dai, Ardern ta iso birnn Beijing, fadar mulkin kasar Sin, kuma wannan shi ne ziyarar aikinta ta farko a kasar Sin, tun bayan da ta zama sabuwar firaministar kasar New Zealand.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China