in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya bar birnin Rome da kyakkyawan sakamakon da aka cimma
2019-03-24 17:10:09 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping a jiya Asabar ya bar birnin Rome na kasar Italiya, bayan kammala tattaunawa da mahukuntan kasar Italiyan tare kuma da halartar taron sanya hannu kan yarjejeniyoyin da aka kulla game da hadin gwiwar bangarorin biyu, ciki har da batun yarjejeniyar fahimtar juna da aka kulla don cimma nasarar shawarar ziri daya da hanya daya.

"Na yi tattaunawar abokantaka mai zurfi da kuma ganawa da jami'an kasar Italiya, ciki har da shugaban kasar," Xi ya bayyana hakan ne a cigaba da ziyarar aikin da yake yi ta kwanaki hudu a kasar Italiya. Kafin ya bar kasar, ya halarci wata gagarumar liyafar girmamawa wanda takwaransa na kasar Italiya Sergio Mattarella, ya shirya masa.

Yana mai cewa, "amincewar juna da kyakkyawar hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin biyu a dukkan fannoni tana kara zurfafa," Xi, ya kuma bukaci kasashen Sin da Italiya dasu kara zurfafa mu'amalarsu domin kara kyautata matsayin alakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China