Wata sanarwa da aka baiwa kamfanin dillancin labarai na Xinhua, Yakubu Sabo, kakakin hukumar 'yan sandan jahar ya bayyana cewa, 'yan bindigar sun shiga kauyen ne inda suka yi awon gaba da shanu masu yawa.
Yace jami'an kungiyar 'yan kato da goran dake kauyen suna bada taimako wajen samar da tsaro da kuma farautar bata gari dake fakewa a cikin dazuka. Sun yi mummunar arangama da 'yan bindigar masu dauke da makamai, lamarin da yayi sanadiyyar rayukan jami'an kungiyar 'yan kato da goran.
Ya kara da cewa, da farko an tsinci gawar 'yan kato da goran 15, kana daga bisani aka sake gano karin gawarwakin mutane biyu.
Kwamishinan 'yan sandan jahar Kaduna Ahmad Abdurrahaman, yayi Allah wadai da kisan sannan ya sha alwashin damke 'yan bindigar da suka aikata kisan.
Abdurrahaman ya bukaci al'umma dasu taimakawa jami'an 'yan sandan wajen basu muhimman bayanai game da duk wasu mutane ko kungiyoyi da basu amince da su ba domin samun nasarar kawar da bata gari a fadin jahar.