in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: Ya kamata a tsaya kan raya harkokin da suka shafi sana'ar noma da karkara gami da manoma
2019-02-20 11:38:42 cri
A kwanakin baya ne, kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin gami da majalisar gudanarwa ta kasar, suka bullo da wasu shawarwari game da tsayawa kan raya harkokin da suka shafi sana'ar noma da yankunan karkara gami da manoma.

Shawarwarin sun ce, bara da bana, muhimman lokaci ne wajen raya zaman al'umma mai matsakaicin karfi daga dukkan fannoni a kasar Sin, kuma a bangarorin sana'ar noma da karkara gami da manoma, akwai jan aiki a gaba. Kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin na ganin cewa, yayin da kasar Sin ke fuskantar matsin bunkasar tattalin arziki da sauye-sauyen yanayin duniya da ake ciki, bunkasa harkoki a wadannan bangarorin uku, wato noma da karkara gami da manoma, na da muhimmanci matuka. Har wa yau, kamata ya yi jam'iyyar Kwaminis mai rike da ragamar mulki a kasar ta tsaya tsayin daka wajen gudanar da ayyuka a wadannan fannoni uku.

Shawarwarin sun ce, ya zama dole a yi azama wajen kawar da fatara a duk fadin kasar Sin, don neman cimma burin yaki da talauci a yankunan karkara, karkashin mizanin da kasar ke amfani da shi yanzu ya zuwa shekara ta 2020.

Bugu da kari, shawarwarin sun ce, ya kamata a inganta tushen sana'ar noma, da tabbatar da samar da isasshen amfanin gona, tare kuma da kyautata tsarin ayyukan gona, da nazarin kimiyya da fasaha a bangaren noma.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China