in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Uganda tana shirin kaddamar da tashar samar da wutar lantarki da kasar Sin ta gina
2019-01-15 20:36:55 cri
Hukumar samar da wutar lantarki ta kasar Uganda (UEGL)ta bayyana cewa, ana nan ana shirye-shiryen kaddamar da tashar samar da wutar lantarki bisa karfin ruwa ta Isimba a yankin tsakiyar kasar da ta ratsa kogin Nilu a ranar 24 ga watan Janairun da muke ciki.

Hukumar wadda ta bayyana hakan cikin wata sanarwa, ta ce a halin yanzu an yi kiyasin cewa, aikin gina tashar mai karfin Megawatt 183 ya kai kaso 98.5 cikin 100.

Tun a shekarar 2015 ne dai aka fara aikin gina tashar, bayan da kasar Uganda ta samu rancen kudi daga bankin shigi da fici na kasar Sin, a wani mataki na magance matsalar wutar lantarki da kasar ke fuskanta, matsalar da kwararru suka ce tana shafar ci gaban tattalin arzkin kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China